Gombe (jiha)

Gombe


Suna saboda Gombe
Wuri
Map
 10°15′N 11°10′E / 10.25°N 11.17°E / 10.25; 11.17
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya

Babban birni Gombe
Yawan mutane
Faɗi 3,256,962 (2016)
• Yawan mutane 173.54 mazaunan/km²
Harshen gwamnati Turanci
Labarin ƙasa
Yawan fili 18,768 km²
Sun raba iyaka da
Bayanan tarihi
Mabiyi Jihar Bauchi
Ƙirƙira 1 Oktoba 1996
Tsarin Siyasa
Majalisar zartarwa executive council of Gombe State (en) Fassara
Gangar majalisa Gombe State House of Assembly (en) Fassara
Bayanan Tuntuɓa
Kasancewa a yanki na lokaci
Lamba ta ISO 3166-2 NG-GO
Wasu abun

Yanar gizo mof.gm.gov.ng
Jihar gombe
Sarkin gombe
gombe post ofis
wajan tirenin a gombe
Governor of Gombe State. Muhammad Inuwa Yahya
Muhammad Damjuma Goje. Passed Governor of Gombe State and Current Senator
Ibrahim Hassan Dankwambo. Passed Governor of Gombe State and Current in House of Assembly
Abubakar Shehu-Abubakar The current Emir of Gombe State
The late Emir of Gombe. His Royal Highness, Alhaji Shehu Usman Abubakar From January 1984 to May 2014
Gombe United FC
President John F. Kennedy visits with members of Parliament of Nigeria in the West Wing Colonnade of the White House, Washington, D.C. The Parliamentary delegation includes: President of the Senate, Dennis Chukude Osadebay; Speaker of the House of Representatives, Ibrahim Jalo Waziri; Deputy Speaker of the House of Representatives, Emmanuel Chikere Akwiwu; members of the Senate, Dahlton O. Asemoto, Chief Z. C. Obi, and Zanna Medalla Sheriff; members of the House of Representatives, Mallam Muhammadu Sagir Umar and Chief Ohu Babatunde Akin-Olugbade; Staff Assistant to the delegation, J. O. Adeigbo.
Sheikh Kabiru Haruna Gombe
Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Amina J. Mohammed
Issa Ali Pantami

Gombe jiha ce dake Arewa maso Gabashin Najeriya. Tayi iyaka daga Arewa da Arewa maso gabas da jihohin Borno da Yobe, daga Kudu kuwa da Jihar Taraba, daga Kudu maso yamma kuwa da Jihar Adamawa sannan daga Yamma da Jihar Bauchi. Ta samo asalin sunanta daga babban birninta kuma yanki mafi girma a jihar wato Babban Birnin Gombe - kuma an ƙirƙireta ne daga sashin Jihar Bauchi a ranar daya ga watan Oktoba shekara ta alif dubu daya da ɗari tara da cassa'in da shida 1996. Jihar na daga cikin jihohin da ke ɗauke da ƙabilu iri-iri a Najeriya. Acikin jihohi talatian da shifa 36, da Abuja na Najeriya, Jihar Gombe itace Jiha ta ashirin da daya 21, a girma, kuma ita ce ta talatin da biyu 32, a yawan jama'a, da mutane aƙalla ya kai kimanian miliyan uku da dugo ashirin da biyar 3.25, dangane da ƙiyasin shekara ta dubu biyu da sha shida 2016.[1]

Ta fuskar yanayin ƙasa, Jihar tana da ƙasa nau'in wuraren zafi a yammacin Sudanian Savanna. Muhimman wurare a jihar sun haɗa Kogin Gongola, wanda ke kwarara ta arewaci da Gabashin Gombe zuwa cikin tafkin Dadin Kowa Dam zuwa gaɓar Tsaunukan Muri da ke can yankin kudancin jihar. Daga cikin dabbobi asali na jihar akwai nau'in macizai addun su: carpet viper, puff adder, da kuma Egyptian cobra da kuma dabbobi irin su dorinar ruwa, Senegal parrot, da kuma grey-headed kingfisher.

Jihar Gombe na ɗauke da ƙabilu da dama, yayinda Ƙabilar Fulani suka mamaye yankin arewaci da tsakiyar jihar tare da Bolewa, Kanuri, da kuma Hausawa. A yayin ƙabilu irin su Cham, Dadiya, Jaranci da Kamo, Pero, Tangavle, Tera, da kuma mutanen Waja da suka mamaye yankunan gabashi da kudancin jihar.

Kafin zuwan Turawa, yankin Jihar Gombe ta yau tana ɗauke da ƙasashe da dama masu zaman kansu, har zuwa farkon karni na dubu daya da dari takwas 1800, lokacin da Fulani suka ƙwace yankuna da dama na yankin kuma suka haɗeta a matsayin Masarautar Gombe a ƙarƙashin Daular Sokoto. A cikin karni na dubu daya da dari tara1900, Turawan mulkin mallaka suka mamaye masarautar da yankunan gefen ta kuma sun haɗeta acikin Yankin Mulkin Mallaka na Arewacin Najeriya, inda daga bayan zuwan turawa Nigeria, daga bisani ta samu 'yancin kai a shekarar dubu daya da dari tara da sittin 1960, kuma ta zamo ƙasa Najeriya. Bayan samun 'yancin kai kuwa, Jihar Gombe ta yau ta faɗa ƙarƙashin Arewacin Najeriya har zuwa shekarar dubu daya da dari tara da sittin da bakwai 1967, lokacin da aka raba yankin kuma jihar ta faɗa ƙarƙashin Jihar Arewa ta Gabas. Bayan an raba Jihar Arewa maso Gabas, an ƙirƙiri Jihar Bauchi a shekarar dubu daya da dari tara da saba'in da bakwai 1976, tare da Sauran jihohi guda goma. Shekaru ashirin bayan haka (1996), an cire wasu gungun ƙananan hukumomi daga yammacin Jihar Bauchi don samar da Jihar Gombe.

Dangane da fannin tattalin arziƙi, Jihar Gombe ta dogara ne akan noma da kiwo, da man fetur, inda ake shuka gero, masara, gyaɗa, dawa da tumatiri tare da kiwon dabbobi kamarsu raƙumma, shanu, akuyoyi da kuma tumaki. Sauran muhimman masana'antu sun haɗa da hidindimu na zamani da ake gudanarwa musamman a birnin Gombe. Jihar Gombe itace jiha ta huɗu a jerin ƙarancin Cigaban al'umma.

Tana da yawan fili kimanin kilomita murabba’i 18,768, da yawan jama’a miliyan biyu da dubu uku da hamsin da uku (ƙidayar yawan jama'a shekara ta dubu biyu da shida 2006). Babban birnin tarayyar jahar ita ce Gombe. Muhammad

Inuwa Yahaya [1] shi ne gwamnan jihar tun zaben shekara ta dubu biyu da sha biyar 2015, har zuwa yau. Mataimakin gwamnan shi ne Dr Manasa Daniel Jatau. Dattijan jihar su ne: Sarakunan gargajiya, Malaman addini da kuma jigogin siyasa.[2]

  1. 1.0 1.1 https://www.britannica.com/place/Gombe-Nigeria
  2. https://www.britannica.com/place/Gombe-Nigeria

From Wikipedia, the free encyclopedia · View on Wikipedia

Developed by Tubidy